Alhamis 5 Maris 2026 - 17:03
A Yanzu Maganar Imam Mahdi (a.s) Ita ce “ Ku Yi Yaƙi da Sahayoniya da Azzaluma Amurka, Jininsu na Kaina"

Hauza/ Ayatullahil Uzma Jawadi Amoli, a cikin wani muhimmin sako, ya bayyana cewa muna fuskantar babbar jarabawa, kuma ya bayyana cewa: "A yanzu maganar Imam Mahdi (a.s) ita ce: “Ku yi yaƙi da 'yan Sahayoniya da Azzaluma Amurka, jininsu na kaina ne.” 

Kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ta ruwaito, Ayatullah al-Uzma Jawadi Amoli, a cikin wani muhimmin sako, ya bayyana cewa babbar al’ummar Iran mai girma da daraja na fuskantar babbar jarabawa, kuma ya yi kira ga kowa da ya kiyaye haɗin kai, da jituwa, da kuma halartar taruka.

Ya bayyana cewa: "Muna sake mika ta’aziyya ga al’ummar musulmi da kuma iyalan mai girma jagoran juyin juya halin Musulunci na shahada mai daraja kuma mai ɗaci. Ya karɓi ladan ɗimbin ayyukansa na tsawon shekaru da shahadar da ke ɗauke da albarka a kan hanyar addini, kuma a yanzu haka yana baƙo a wurin Sayyidus Shuhada da kuma Imam Hassan ibn Ali (AS)."

Ya ci gaba da cewa: "Haka kuma muna taya murnar shahadar wasu manyan kwamandandoji da manyan shugabannin harkokin soja, muna mika ta’aziyya ga iyalansu masu daraja. Haka nan, ina taya dukkan shahidai 'yan ƙasa masu daraja da suka sadaukar da kansu don kare addinin Musulunci da kasarmu ta Musulunci kuma suka samu tagomashin shahada da ni’imar bin tafarkin annabawan Allah, shahadarsu ta kasance mai albarka. Ina kuma mika ta’aziyya ga iyalai da waɗanda suka rage na waɗannan jarumai."

Ya ci gaba da cewa: "Muna kuma mika ta’aziyyar shahadar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da yara marasa laifi na makarantar Minab. Shahadar waɗannan yara masoya da hasken idanuwanmu daga makarantar Minab da sauran makarantun da suka dandani ɗanɗanon shahada tun suna ƙananan yara ‑ muna mika ta’aziyya ga iyalan su masu girma da girmamawa. Sannan da duk wanda jininsu ya zuba a wannan hanya, wanda ya sami martabar shahada, Allah ya haɗa su da shahidan Karbala da shahidan da ke kan tafarkin gaskiya."

Ayatullah al-Uzma Jawadi Amoli ya bayyana cewa: "Duk wanda ya mutu a kan tafarkin gaskiya, wanda ya mutu saboda addini, tabbas zai tashi tare da dukkan annabawa a Lahira." Ya ƙara da cewa: "Idan mawakanmu na baya sun ce: “Ina yabawa ga hannun da ya shuka inabi, kuma ga tafin da ya matse shi.” To waƙar yau ita ce: “Ina yabawa ga hannun da ya kera makami (roka), kuma ga hannun da yake harba shi.” Na faɗa sau da dama game da waɗannan masanan da ke ƙera makamai — “Amincin Allah a gare su” — su ne mafi kyawun masu taimako ga Waliyyul Asr. Kamar yadda sahabban Imamai (a.s) na musamman suka kasance mataimakansu, waɗannan su ma masu taimako ne ga jagoransu, ga Jamhuriyyar Musulunci ta Iran da al’umma baki ɗaya."

Ya ci gaba da cewa: "Muna kuma taya murnar shahadar wasu manyan kwamandandoji da manyan shugabannin harkokin soja, kuma muna mika ta’aziyya ga iyalansu masu daraja. Haka nan, ina taya dukkan shahidan 'yan ƙasa masu daraja da suka sadaukar da kansu don kare addinin Musulunci da kasarmu ta Musulunci kuma suka samu tagomashin shahada da ni’imar bin tafarkin annabawan Allah, shahadarsu ta kasance mai albarka. Ina kuma mika ta’aziyya ga iyalai da waɗanda suka rage na waɗannan jarumai."

Mai girma Ayatullah Jawadi Amoli ya kawo hadisin Imam Sadiq (a.s):

“من قُتِلَ دُونَ مالِهِ ظُلْمًا فَهُوَ شَهِيدٌ”

— “Duk wanda aka kashe saboda kare dukiyarsa da zalunci, shahidi ne.”

Wannan shi ne tsarin addini. Lokacin da aka tambayi Imam Ma’asum; Idan wani ya yi niyyar kwace mana ƙasar mu, dukiyar mu, ko mutuncin mu, me za mu yi? Sai ya ce: “Ku kashe shi — jinin sa na kaina ne.” Wato: “Zubar da jinin Sahayoniya (Zionist) ko Trump da makamantansu — jinin su na kaina ne.” Yanzu maganar Imam Mahdi (a.j) ita ce: Ku yi yaƙi da Sahayoniya, jinin su a kaina yake."

Ayatullah al-Uzma Jawadi Amoli ya yaba da tsayuwar al’ummar Iran masu girma a fagen gwagwarmaya, da cewa su ne masu kiyaye addinin Allah. Ya ce: "Ina ganin girman ku, ya ku al’ummar Iran masu girma, waɗanda date da rana ba su bar filin gwagwarmaya ba. Muna mika godiya ga ‘yan uwanmu mata, iyaye, ‘ya’ya mata, maza, uba da ‘ya’ya maza. Amincin Allah, Annabi , Ali ibn Abi Talib, Imam Sadiq da Imam Mahdi gare ku, domin ku ne masu kiyaye addininsa."

Ya ƙara jaddada bukatar kiyaye haɗin kai, yana cewa: "Ku mutane masu girma da daraja ne — ku kiyaye wannan haɗin kai. Bambanci na ra’ayi abu ne mai albarka, amma sabani da gaba abu ne mai muni. Alƙur’ani yana kiran bambanci ni’ima, amma yana kiran gaba da azaba."

A ƙarshe, ya roƙi Allah ya kiyaye tsarin juyin juya halin Musulunci da gwamnati, yana cewa: "Ina fatan shahidai gaba ɗaya, musamman Jagoran shahidan (Jagoran Juyin Juya Hali), su kasance baƙi a wajen Husain ibn Ali (a.s) da sauran shahidai, kuma wannan tsarin ya kasance lafiya har sai an miƙa shi ga Mai shi — Waliyyul Asr (a.j). Yanzu watan Ramadan ne, lokacin karɓar addu’o’i. Muna godiya wajen mata, maza, ‘yan uwa, waɗanda suka yi ƙoƙari ba tare da dimaucewa su bar filin ba, suna nan suna tallafa wa juyin juya hali — ladansu yana tare da Allah Maɗaukaki."

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha